in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na kan matsaya mai kyau game da batun kawar da makaman nukiliya a zirin Koriya
2017-05-04 20:45:09 cri
A Alhamis din nan ne kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya yi tsokaci game da bayanin da kamfanin dillancin labaru na Koriya ta Arewa ya yi, yana mai cewa Sin ta dauki matsaya mafi dacewa, game da batun kawar da makaman nukiliya a zirin Koriya, da raya dangantakar dake tsakanin Sin da Koriya ta Arewa.

Mr. Geng wanda ya amsa a gun taron manema labaru da aka gudanar a wannan rana, akwai tambaya cewa, mene ne ra'ayin Sin game da bayanin da kamfanin dillancin labaru na Koriya ta Arewa ya bayar inda ya zargi Sin da ta yi matsin lamba ga sakawa kasar Koriya ta Arewa takunkumi?

Geng Shuang ya bayyana cewa, Sin ta tsaya tsayin daka kan manufar kawar da makaman nukiliya a zirin Koriya da tabbatar da zaman lafiya da na karko a zirin, da sa kaimi ga warware batun ta hanyar yin shawarwari. Sin tana fatan bangarori daban daban da abin ya shafa za su dauki alhakinsu da taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya da rayuwar jama'a a yankin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China