in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi: kasar hadaddiyar daular Larabawa ba za ta zama mafaka ga masu cin hanci na kasar Sin ba
2017-05-02 20:48:44 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, da ministan harkokin waje da hadin gwiwar kasa da kasa na kasar hadaddiyar daular Larabawa Sheikh Abdullah Bin Zayed Al Nahyan dake ziyara a nan birnin Beijing na kasar Sin, a yau Talata sun gana da 'yan jarida tare, bayan taron kwamitin hadin gwiwa tsakanin gwammatocin Sin da hadaddiyar daular Larabawa karo na farko.

A yayin taron, Wang Yi ya bayyana cewa, Sin ta gabatar da batun yaki da cin hanci da rashawa, da kudurin ta na cafke 'yan kasar ta da suka aikata laifin cin hanci ko al'mundahanar kudade. Matakin da ya samu goyon baya daga hadaddiyar daular Larabawa.

Mr. Wang ya kara da cewa, kasashen biyu na hadin gwiwa wajen aikin mika mutanen da suka aikata laifi a kasar Sin, kana ya yi imanin cewa, hadaddiyar daular Larabawa, ba za ta zama mafaka ga wadanda suka aikata cin hanci a kasar Sin ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China