in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Fiye da kashi 51 cikin dari na masu jefa kuri'u a Turkiya sun amince da gyara kundin tsarin mulkin kasar
2017-04-17 11:10:26 cri
Bisa sakamakon kidaya kuri'un da aka jefa da kamfanin dillancin labaru na Anadolu na kasar Turkiya ya gabatar a ranar 16 ga wata, an ce, a zaben jin ra'ayoyin jama'a da aka yi a kasar, kimanin kashi 51.35 cikin dari na masu jefa kuri'un sun amince da a yi gyaran kundin tsarin mulkin kasar. Shugaban kasar Turkiya Recep Tayyip Erdogan, ya sanar a daren ranar 16 ga wata cewa, an zartas da daftarin gyara kundin tsarin mulkin kasar a zaben a wannan rana.

A zaben jin ra'ayoyin jama'a da aka yi, ya shafi kudurin doka ta 18 na gyara kundin tsarin mulkin kasar, ciki har da kudurin canja tsarin kasar daga tsarin majalisar dokoki zuwa tsarin shugaba wanda shi ne ya fi jawo hankali sosai. Bisa daftarin gyara kundin tsarin mulikin kasar, za a kafa mukamin mataimakin shugaba guda biyu, kana shugaban kasar zai iya nada mataimakin shugaba da ministocin gwamnatin kasar, kana shugaban kasar zai iya ci gaba da zama shugaban jam'iyyarsa, da a soke mukamin firaministan kasar. Za a kara baiwa shugaban kasar ikon a cikin kundin tsarin mulkin kasar da za a gyara.

Hukumar zaben kasar Turkiya za ta gabatar da sakamakon kidaya kuri'un zaben a hukumance a cikin mako daya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China