in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu kai tsegumi na kara karfafa yaki da cin hanci hanci da rashawa a Nijeriya
2017-04-14 10:47:39 cri
Yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya na kara samun nasara, inda masu bada tsegumi a baya-bayan nan, ke bankado makudan kudade da asusun ajiya ga hukumomi, musammam ma hukumar dake yaki da masu cin hanci da rashawa.

A kwanan nan ne, gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta yanke shawarar yaki da cin hanci ta hanyar amfani da masu tsegumi a matsayin wata sabuwar dabara.

Wannan mataki, zai ba jama'a damar bada rahoto ta wata kafa cikin sirri, inda za su samu wani kaso daga cikin kudaden da aka kwato.

Masu tsegumin za su samar da bayanai ga hukumomi kamar EFCC mai yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa tu'annuti, ta yadda za su taimaka musu wajen kwato kudaden gwamnati da aka yi sama da fadi da su.

Laifukan da za a iya kai rahotonsu sun hada da sace kudade da kadarorin gwamnati, da take ka'idojin hada-hadar kudade, da neman na goro da kuma sauya bayanai.

Idan har tsegumin ya kai ga nasarar samo kudaden da aka yi sama da fadi da su, to wanda ya tseguntawa hukumomi zai samu tukwicin tsakanin kashi 2.5 zuwa kashi 5 na kudin.

Gwamnatin dai ta yi alkawarin tabbatar da kare sirrin masu tsgeunta mata kamar yadda doka ta tanada.

Zuwa yanzu dai, dabarar ta tseguntawa hukumomi na aiki a Nijeriya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China