in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin Masar ta amince da kafa dokar ta baci ta watanni 3
2017-04-12 10:42:36 cri
A jiya Talata majalisar dokokin kasar Masar ta amince da kafa dokar ta baci na tsawon watanni 6, kwanaki biyu bayan harin da aka kaddamar kan wata cocin a kasar wanda ya hallaka mutane 45.

A ranar Litinin ne majalisar zartarwar kasar Masar ta sanar da kafa dokar ta bacin da misalin karfe 1 na rana, sai dai ta ce dole ne ta bukaci amincewar majalisar dokokin kasar kamar yadda dokar kundin tsarin mulkin kasar ta tanada.

Shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-Sisi ya bayyana dokar tabacin ne yayin wani jawabi ta gidan talabijin din kasar bayan harin na ranar Lahadi.

Ya ce an dauki wannan mataki ne domin samar da kariya da tsaron kasar domin gujewa yiwuwar kai karin wasu hare haren.

Cikin wani bayani da ya gabatarwa majalisar wakilan kasar, firaiministan kasar Sherif Ismail, ya bukaci a kara daukar matakan yaki da ta'addanci a kasar ta Masar.

A ranar Lahadin da ta gabata ne, wasu tagwayen boma bomai na yan kunar bakin wake suka kaddamar da hari kan coci biyu dake lardunan Gharbiya da Alexandria a arewacin kasar ta Masar inda suka hallaka mutanet 45 da rauna wasu 120. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China