Tuni dai aka garzaya da mutanen da suka jikkatan zuwa wani asibiti dake kusa don yi musu magani, a yayin da aka kuma tsaurara matakan tsaro tare da killace wajen da harin ya afku, kuma motocin daukar marasa lafiya sun isa wurin cikin gaggawa.
Kasar Masar dai ta sha fama da hare-haren ta'addanci da suka hallaka daruruwan 'yan sanda da sojoji tun bayan da sojojin suka hambarar da tsohon shugaban kasar Mohamed Morsi a watan Yulin shekarar 2013.