in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na tsayawa kan matsayin nuna goyon baya ga kokarin hana da rushe dukkan makaman nukiliya kwata kwat
2017-03-20 19:44:38 cri
A yau a wani taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing, mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying, ta bayyana cewa, ko da yake kasar Sin ba za ta tura wakilinta zuwa taron tattaunawa kan "yarjejeniyar hana makaman nukiliya" da za a yi nan ba da dadewa ba, amma ko shakka babu bangaren Sin, bai canja matsayinsa na nuna goyon baya ga kokarin hana, da kuma rushe dukkan makaman nukiliya gaba daya ba.

Za dai a shirya kira taron tattaunawa kan "yarjejeniyar hana makaman nukiliya" a birnin New York a ran 27 ga watan nan da muke ciki. Game da hakan ne kuma, a yayin taron manema labaru da aka shirya yau Litinin, da take ba da amsa ga tambaya game da ko kasar Sin za ta halarci wannan taro ko a'a? Hua Chunying ta ce, har kullum bangaren Sin yana mu'amala, da musayar ra'ayoyinsa ba tare da boye kome ba, da dukkanin bangarorin masu ruwa da tsaki.

Ta ce bisa nazarin da aka yi cikin taka tsantsan, bangaren Sin ya tsai da kudurin cewa, ba zai halarci wannan taro ba. Dalilin da ya sa hakan kuwa shi ne, Sin na fatan za a kiyaye ka'idojin jan damara, da rage yawan sojoji, da makamai da ake bi yanzu, tare da fatan gudanar da hakan sannu a hankali. Wannan kuduri ya bayyana yadda kasar Sin ke sauke nauyin da ke bisa wuyansa, na tabbatar da daidaito da kwanciyar hankali tsakanin kasa da kasa. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China