in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta fara sintirin sa ido ta sama dan tabbatar da tsaron matafiya
2017-03-12 12:48:35 cri
Rundunar 'yan sandan Nijeriya, ta ce ta fara sintirin sa ido ta sama ba dare ba rana tsawon sa'o'i 24, a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna dake yankin arewa maso tsakiyar kasar, biyo bayan karuwar zirga-zigar ababen hawa a kan titin.

Mataimakin babban Sufeton 'yan sanda dake Abuja, babban birnin kasar Salisu Fagge, ya ce matakin wani bangare ne na tabbatar da tsaron lafiyar matafiya dake bin titin.

Ya ce ana sa ran samun karuwar zirga-zirgar ababen hawa akan titin nan da makonni shida masu zuwa, saboda mai da zirga zirgar jiragen sama da aka yi daga filin jirgin saman kasa da kasa na Nnmadi Azikwe dake Abuja zuwa filin jirgin saman Kaduna.

An rufe filin jirgin saman Abuja ne a ranar Laraba da ta gabata saboda wasu muhimman gyare-gyare da za a aiwatar, musammam ma akan titin jirgi.

Ya kara da cewa, an umarci kwamishinonin 'yan sanda na jihohin Kaduna da Niger da kuma na birnin Tarayya Abuja su dauki dukkan matakan da suka dace na kawar da duk wata barazanar tsaro akan titin da sauran wurare. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China