in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Italiya ta mai da wasu 'yan Nijeriya 37 gida bisa zarginsu da aikata laifukan da suka shafi shige da fice
2017-03-09 09:39:14 cri
Rundunar 'yan sandan Nijeriya ta ce Kasar Italiya, ta tasa keyar wasu 'yan kasar 37, bisa zarginsu da aikata laifukan da suka shafi shige da fice.

Kakakin Rundunar 'yan sandan jihar Lagos dake kudu maso yammacin kasar Joseph Alabi, ya ce 'yan Nijeriyar da a aka mai da gida, sun isa Lagos din ne da yammacin ranar Talata, kasa da makonni biyu ke nan, bayan hukumomin Italiyar sun mayar da wasu 'yan kasar 33 bisa zarginsu da aikata makamancin wancan laifi.

Jami'an hukumar kula da shige da fice na kasar da takwarorinsu na hukumar yaki da safarar bil'adama da na rundunar 'yan sanda ne suka karbi mutanen da suka kasasnce maza duka.

Jami'an hukumar shige da fice ne suka dauki bayanansu, kana suka shirya yadda za a mai da su garuruwansu.(Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China