in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kasar Sin sun tattauna da 'yan majalisu kananan kabilu dake halartar tarruka biyu
2017-03-12 13:37:01 cri
A daren jiya Asabar ne a dakin taron jama'a da ke nan birnin Beijing, shugabannin kasar Sin, ciki har da shugaban kasa Xi Jinping, da firaminista Li Keqiang suka hadu da 'yan kananan kabilu na majalisar wakilan jama'a da na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasar kasar wadanda ke halartar tarukan majalisun biyu da har yanzu ke gudana a nan birnin Beijing, don tattaunawa tare da su.

A yayin tattaunawar, shugabanni sun ba 'yan majalisun kwarin gwiwar sauke nauyin dake wuyansu yadda ya kamata, tare da kara himmantuwa wajen ba da shawarwari ga kasa, da gudanar da ayyuka a fannonin inganta yin kwaskwarima, neman ci gaba, inganta walwalar jama'a, da kuma hada kan jama'ar kabilu daban-daban don kokarin cimma burin farfado da al'ummar kasar Sin.

Tun bayan babban taron wakilai karo na 18 na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, kwamitin tsakiyar jam'iyyar ya mayar da hankali sosai kan ayyukan kananan kabilu, da kuma bunkasar yankunan kabilun.

Shugaba Xi Jinpin sau da yawa ya kai rangadi a yankunan kabilu, don fahimtar yadda rayuwar jama'a kananan kabilu ya ke, tare da kuma tsara shirin inganta rayuwarsu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China