in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An samu mutane 63,000 da laifi a shari'u kan laifukan cin hanci 45,000 da kotunan kasar Sin suka kammala a shekarar 2016
2017-03-12 12:21:41 cri
Rahoton ayyuka na kotun kolin jama'ar kasar Sin, ya ce kotunan kasar, sun kammala shari'un cin hanci 45,000 a cikin shekarar 2016, inda aka samu mutane 63, 000 da laifi.

Babban jojin kasar Sin Zhou Qiang, wanda ya bayyana haka yayin da yake gabatar da rahoton bangaren shari'a ga taron majalisar wakilan jama'ar kasar Sin NPC, ya ce daga cikin wadanda aka tuhuma yayin shari'un sun har da da tsoffin ministoci da jami'ai a matakin larduna guda 35 da wasu 240 a matakin yankuna .

Tun lokacin babban taron wakilan Jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin a shekarar 2012 ne kasar Sin ta kaddamar da gagarumin yaki da cin hanci da rashawa, inda a karshen shekarar da ta gabata ne shugabancin jam'iyyar ta sanar da cewa shirin ya samu dimbin nasarori.

A cewar rahoton da mai gabatar da kararraki a kotu na kasar Sin ya gabatar, a cikin shekarar 2016, hukumomin gabatar da kararraki sun gudanar da bincike kan mutane 47,650 da ake zargi da aikata laifuka da suka danganci gudanar da ayyukansu.

hukumomin sun kuma gudanar da bincike kan wasu kananan jami'ai 17, 410 da ake zargi da aikata cin hanci a fannonin daban-daban da suka shafi kyautata rayuwar al'umma. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China