in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sudan da shirin UNDP na MDD sun kaddamar da wani shiri na yaki da tsattsaurarn ra'ayi
2017-03-10 09:56:52 cri
Hukumar yaki da ayyyukan ta'addanci ta kasar Sudan da hadin gwiwar shirin samar da ci gaba na MDD wato UNDP, sun kaddamar da wani shiri mai yaki da tsattsauran ra'ayi da aka yi wa lakabi da PAVE.

Firayiminista kuma mataimakin shugaban kasar na daya Bakri Alhassan Saleh da wasu jami'an gwamnati da na hukumar yaki da ayyukan ta'addanci ta kasar da jami'an MDD da na kungiyoyin bada agaji da hukumomin da abun ya shafa da na kungiyoyin al'umm da shugabannin addinai da kungiyoyin matasa dake cikin masu samar da dabarun yaki da tsattsauran ra'ayi a Sudan, na daga cikin wadanda suka shaida kaddamar da shirin a jiya Alhamis.

Firayiminista kuma mataimakin shugabn kasar na daya, Bakri Hassan Saleh ya jadadda kudurin gwamnatin Sudan na bada hadin kai wajen yaki da tsattsauran ra'ayi a kasar.

A nata bangare, Shugabar shirin bada agajin jin kai na MDD kuma shugabar shirin UNDP a Sudan Marta Ruedas, ta ce ba kadai Sudan ayyukan masu tsattsauran ra'ayi ya shafa ba, har da nahiyar da ma duniya baki daya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China