Wata sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen Sudan din ta fitar, ta ruwaito mataimakin sakataren ma'aikatar harkokin wajen na bayyana takaicin kasar ga jakadan Amurka Steven Koutis game da haramtawa 'yan asalin kasar shiga Amurka.
Sanarwar ta ce Sudan na jiran Amurka ta cire ta daga jerin kasashen dake daukar nauyin ta'addanci, ta na kuma mai kira a gare ta, da su hada hannu wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro da kuma ci gaba.
Sudan din ta kara da cewa, za ta ci gaba da bada hadin kai a kokarin da ake na shawo kan ayyukan ta'addanci tare da cimma tsaro da zaman lafiya a yankin da take da ma duniya baki daya. (Fa'iza Mustapha)