in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sabuwar gwamnatin Sudan za ta kunshi duk 'yan siyasar kasar, in ji al-Bashir
2017-03-03 10:55:55 cri
Shugaba Omar al-Bashir na kasar Sudan ya bayyana cewa, sabuwar gwamnatin kasar da ake fatan kafawa za ta kunshi dukkan bangarorin siyasar kasar, sai dai kuma bai yi karin haske game da ranar da za a kafa gwamnatin ba.

Shugaba al-Bashir ya kuma shaidawa taron manema labarai cewa, ana ci gaba da tattaunawa don ganin an cimma matsaya game da mukaman da za a raba a dukkan matakai.

Ya kuma lashi takwabin cewa, jam'iyyar NCP mai mulkin kasar za ta ba da hadin kai don tabbatar da cewa, an kafa gwamnatin da za ta kunshi dukkan bangarorin siyasar kasar.

Sabon firaministan kasar ta Sudan Bakri Hassan Saleh ne zai jagoranci aikin sake fasalta hukumomin gwamnatin kasar.

A jiya Alhamis ne dai sabon firaminsitan na Sudan ya sha rantsuwar kama aiki.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China