in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta ce sama da 'yan gudun hijirar Sudan ta kudu 31,000 ne suka isa Sudan cikin watannin Junairu da Fabreru
2017-03-01 10:33:13 cri
Ofishin babban kwamishinan hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD, ya ce sama da 'yan gudun hijira na kasar Sudan ta Kudu 31,000 ne suka isa Sudan, cikin watanni biyu na farkon shekarar nan.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta ce da farko, anyi hasashen samun 'yan gudun hijira 60,000 cikin shekarar 2017, amma cikin watanni biyu na farkon shekarar kawai, an samu adadin da ya zarce 31,000.

Sanarwar ta yi bayanin cewa, kiyasin da aka yi da farko, ya nuna cewa, kashi 80 cikin sabbin zuwan mata da yara ne, ciki har da yara da suka rabu da iyayensu, ta na mai cewa, suna tsananin bukatar taimako, da hukumar ta kula da 'yan gudun hijira da sauran hukumomin kawayenta, ke kokarin samarwa.

Wakiliyar hukumar a kasar Sudan, Noriko Yashida, ta fada cikin wata sanarwa cewa, sun damu matuka da halin da mutanen ke ciki, musammam yara da su ne suka fi wahala. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China