in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin PowerChina ya kafa babbar hedikwatarsa a Kenya
2017-03-09 11:19:49 cri

Jiya Laraba, wani babban kamfanin kasar Sin wato PowerChina ya kafa babbar hedikwatarsa mai kula da harkokin kudu maso gabashin Afirka a birnin Nairobin Kenya, lamarin da ya kasance wani sabon ci gaban da wannan kamfani ya samu ta fannin gudanar da ayyukansa a nahiyar Afirka.

Ministan kudin Kenya Henry Rotich, da jakadan kasar Sin dake Kenyar Liu Xianfa, da mataimakin babban manajan kamfanin PowerChina Wang Bin ne suka halarci bikin bude kamfanin.

Mista Henry Rotich ya bayyana cewa, kasar Sin muhimmiyar aminiya ce ta Kenya, kuma hadin-gwiwar kasashen biyu ta fuskar tattalin arziki na kara ingantuwa. Mista Henry ya ce, kafa babbar hedikwata a Kenya da kamfanin PowerChina ya yi, na nuni da irin karfin dangantaka dake tsakanin kasashen biyu.

A nasa bangaren, jakada Liu Xianfa ya ce, kamfanin PowerChina ya bayar da babbar gudummawa a fannin raya Afirka gami da kyautata zamantakeware mutanen nahiyar.

Liu ya kuma yi fatan kamfanin PowerChina zai ci gaba da kokarinsa na kyautata harkokin da yake gudanarwa a Afirka, da kara karfafa hadin-gwiwa tsakanin kasashen biyu.

Rahotanni sun bayyana cewa, PowerChina, wani hamshakin kamfanin kasar Sin ne dake gudanar da ayyukan da suka shafi makamashi, wutar lantarki, ayyukan more rayuwar al'umma, ruwa, muhalli da sauransu. Tuni dai wannan kamfani ya kafa hedikwatarsa a yankin Asiya da Pasific, da kuma yankin tsakiya da yammacin nahiyar Afirka.

Wannan sabuwar hedikwatar da kamfanin ya kafa a kasar Kenya, zai kula da ayyukan da suka shafi kasashe 26, ciki har da Kenya, Habasha, Uganda, Tanzaniya, Zambiya, Zimbabwe, Afirka ta Kudu da sauransu.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China