in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babbar kotun Kenya ta dankwafe yunkurin gwamnatin kasar na rufe sansanin 'yan gudun hijira na Dadaab
2017-02-10 10:01:06 cri
Babbar kotun kasar Kenya ta dankwafe matakin gwamnatin kasar na rufe sansanin 'yan gudun hijira na Dabaab, da galibin 'yan kasar Somalia ke samun mafaka, tana mai bayyana matakin na gwamnati da sabawa kundin tsarin mulki.

A hukuncin da ya yanke, Alkalin kotun John Mativo ya bayyana umarnin da babban sakataren ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar, Joseph Nkaissery da takwaransa na fadar shugaban kasa, Karanja Kibicho suka bayar a matsayi maras dalili.

Mativo ya ce umarnin gwamnatin na mayar da 'yan gudun hijirar da ke samun mafaka a sansanin da shi ne mafi girma a duniya, nuna wariya ne da ka iya janyo mayar da martini, yana mai bayyana shi a matsayin mai tsauri da bai dace ba

Ya kara da cewa, babu wata shaida da ke nuna cewa, mutanen sun taba aikata wani laifi, ko kuma kotu ta taba yankewa wani daga cikinsu hukunci, sannan babu shaidar dake cewa akwai 'yan kungiyar Al shabaab a sansanin.

Alkalin ya kuma umarci gwamnati ta dauki matakan da za su tabbatar da sashin da ke kula da 'yan gudun hijira na aiki yadda ya kamata, sannan ta kauracewa nunawa 'yan gudun hijira wariya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China