in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kira taron tattaunawa kan hadin kan majalisun dokokin kasashen Sin da Masar
2017-03-07 12:41:57 cri
A jiya Litinin a birnin Alkahira na kasar Masar, an shirya taron tattaunawa kan hadin kan majalisun dokokin kasashen Sin da Masar da makomarsu a nan gaba. Jakadan kasar Sin dake Masar Song Aiguo ya halarci taron, tare kuma da yin jawabi.

A yayin jawabinsa, jakada Song ya bayyana cewa, yanzu haka ana gudanar da manyan taruka biyu na kasar Sin a birnin Beijing, wato taron shekara shekara na majalisar wakilan jama'ar kasar, da na majalisar ba da shawara kan harkokin siyasar kasara. Yayin tarukan biyu na bana, za a dudduba rahotanni guda 6, ciki har da rahoton ayyukan gwamnati, inda 'yan majalisun za su ba da shawarwari kan manyan batutuwan da suka shafi harkokin kasa da na zaman rayuwar jama'a, a sa'i guda za su taka rawa wajen kafa dokoki da sa ido.

Jakada Son ya kara bayyana cewa, ofishin jakadancin kasar Sin dake Masar, na fatan ci gaba da karfafa mu'amala, da hadin kai tare da majalisar dokikin masar, yana kuma mai fatan inganta manufar ziyarar juna a matakai daban daban a tsakanin majalisun dokokin kasashen biyu, da karfafa cudanya tsakanin kwamitocin musamman na majalisun biyu, da nufin ciyar da kyakkyawar dangantakar hadin su gaba.

'Dan majalisar dokokin kasar Masar Nader Mostafa ya bayyana cewa, yin mu'ammala tsakanin majalisun dokoki muhimmiyar hanya ce, ta karfafa dangantakar hadin kai tsakanin kasashen biyu.

A shekarun baya bayan nan, an kara daukar matakan karfafa cudanya, da ziyartar juna a tsakanin sabuwar majalisar dokokin Masar da majalisar wakilan jama'ar kasar Sin, matakin da zai zurfafa hadin kai da amincewar juna a tsakaninsu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China