in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun Aljeriya sun gano makaman yaki kusa da kan iyakar kasar
2017-03-06 09:36:00 cri
Ma'aikatar tsaron kasar Aljeriya, ta ce dakarun sojin kasar masu yaki da ayyukan ta'addanci, sun gano wasu tarin makaman yaki a kusa da kan iyakar kasar da janhuriyar Nijar. Rahotanni sun bayyana cewa, an bankado makaman ne a wata maboya ta karkashin kasa dake Guezzam, a kusa da kan iyakar kasar ta kudu.

Tuni dai mahukuntan Aljeriya suka jibge dakarun tsaro har 10,000 a yankin dake kudancin iyakar kasa, a wani mataki na dakile kwararar mayakan kungiyoyin ta'addanci, da makamai daga wasu kasashe makwaftan ta.

A baya bayan nan dai an gano wurare da dama, wadanda mayakan sa kai ke boye makamai a kan iyakokin kasar da kasashen Mali, da Nijar da Libya, an kuma hallaka tare da kame 'yan ta'adda da dama yayin simame da sojin kasar ke kaddamarwa.

Kwararru ta fuskar tsaro na cewa, Aljeriya na yanki mai tattare da kalubalen tsaro, da yanayin siyasa maras tabbas, don haka dole ta dauki kwararan matakai, na dakile aukuwar hare hare daga 'yan ta'adda.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China