in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya yi kira ga bangarori daban daban na yankin yammacin hamadar Sahara da su yi hakuri da juna
2017-02-26 17:12:56 cri
Babban sakataren MDD António Guterres ya fitar da wata sanarwa ta bakin kakakinsa a jiya Asabar, inda ya ce, ya damu sosai da halin da ake ciki a yankin yammacin hamadar Sahara a baya bayan nan, yana mai kalubalantar bangarori daban daban dake yankin da su yi hakuri da juna.

Sanarwar ta bayyana cewa, a kwanakin baya, an tsananta halin da ake ciki a yankin iyakar kasa a tsakanin Morocco da Mauritania dake kudancin yankin yammacin hamadar Sahara, dakarun Morocco da na jam'iyyar 'yantar da jama'ar yammacin Sahara sun nuna adawa da juna a wadannan watannin da suka gabata.

Guterres ya ce ya damu sosai da batun, inda ya kalubalanci bangarorin biyu da su yi hakuri da juna, tare da daukar matakai da suka dace domin shawo kan matsalar.

Haka zalika, Guterres ya kalubalanci bangarorin biyu da su janye sojoji daga yankin iyakar kasar, tare da samar da hanyoyin hawa teburin sulhu da kuma tabbatar da bin yarjejeniyar tsagaita bude wuta. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China