in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Afrika ta Kudu ya bukaci al'ummar kasar su dai na dora alhakin laifukan da ake aikatawa akan baki
2017-02-25 12:43:33 cri
Shugaban kasar Afrika ta Kudu Jacob Zuma, ya roki al'ummarsa kada su dorawa baki alhakin laifukan da ake aikatawa a kasar.

A daidai lokacin da wata sabuwar zanga-zangar kin jinin baki ta barke a wasu garuruwa na kasar, Jacob Zuma ya ce galibin bakin da ke zaune a kasar suna kiyaye doka da oda, sannan suna bada gudunmuwa ga habakar tattalin arzikin kasar.

A jawabin nasa na jiya, ya ce kuskure ne yi wa bakin daurin goro, inda ake alakantasu da safarar miyagun kwayoyi ko na bil'adama.

Sai dai, ya ce al'ummar kasar a yankuna daban-daban sun damu matuka da laifukan da ake aikatawa, wadanda ke tada hankalin al'ummomi.

A farkon watan nan ne zanga-zangar kin jinin baki ya barke a Pretoria ta yamma da kuma Rosenttenville.

Haka zalika al'amura na kara tsanin ta wasu bangarori, ciki har da musayar kalmomin batanci da na barazana a shafukan intanet.

Jacob Zuma ya yi suka da kakausar murya, kan duk wani nau'i na zanga-zanga, ya na mai kira da baki a kasar su kara hakuri, su kuma guji aikata laifuka, sannan, su yi aiki da hukumomin da suka dace domin tabbatar da hukunta wadanda ke aikata laifuka. ( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China