in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban editan Xinhua ya nuna yabo kan dangantakar sadarwa tsakanin kasashen BRICS
2016-08-27 12:24:12 cri
Dangantaka tsakanin hukumomin aikin jarida na kasashen BRICS na taimakawa tattalin arzikin kasashen masu tasowa wajen kara karfin fada-a-jinsu a duniya, in ji He Ping, babban editan kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua a ranar Jumma'a.

Kasashen BRICS na wakiltar muhimman tattalin arzikin kasashe masu tasowa guda biyar na duniya wato Brazil, Rasha, Indiya, Sin da Afrika ta Kudu.

Dangantakarsu a bangaren watsa labarai na iya taimakawa wajen kafa wani sabon tsarin duniya na sadarwa bisa adalci, in ji mista He.

Ya gaya ma Xenia Fedorova, daraktar kamfanin dillancin labarai na Ruptly, cewa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a shiye yake wajen karfafa dangantakarsa tare da kafofin watsa labarai na kasar Rasha, domin bunkasa fahimtar juna da abokantaka.

Ruptly, wani reshen Russia Today (RT), ya kasance wata hukumar dillancin watsa labaran kasa da kasa dake da hedkwata a birnin Berlin na kasar Jamus. Yana harhada rahotannin bidiyo kai tsaye bisa lokaci da kuma hotunan tarihi ga dukkan kafofin watsa labarai. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China