in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Adadin mutanen da suka rasu sakamakon harin da aka kai a Pakistan ya karu zuwa 88
2017-02-18 13:34:01 cri
Wani jami'in kiwon lafiya a jihar Sind ta kasar Pakistan, ya bayyana a jiya Jumma'a cewa, ya zuwa yanzu, harin kunar bakin wake da aka kai wani wurin ibada a yankin Sehwan na lardin Sind a daren ranar 16 ga wata, ya haddasa mutuwar mutane 88 tare da raunatar wasu 343.

Bisa binciken da aka gudanar, an gano cewa, maharin ya yi ado irin na 'yan mata mazauna yankin, inda ya shiga wajen ibadar tare da tada bam din da ke jikinsa mai nauyin kilo 7.

Gwamnatin lardin Sind, ta ayyana ranar 17 zuwa 19 ga wata, a matsayin ranar zaman makoki, inda za kuma a yi kasa-kasa tutoci domin nuna alhinin mutuwar da kuma mutanen da harin ya rutsa da su.

Tun daga ranar 17 ga wata ne, aka fara aikin kama 'yan ta'adda a duk fadin kasar ta Pakistan, inda aka karfafa matakan tsaro, musamman a wasu wuraren da aka fi kai harin ta'addanci, sannan, za a rufe wuraren ibada cikin dan lokaci. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China