in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin AU: Zaben sabon shugaban Somaliya zai bude sabon babin ci gaba
2017-02-16 09:48:19 cri
Wakilin musamman na shugaban hukumar zartarwar kungiyar tarayyar Afirka mai kula da kasar Somaliya Francisco Madeira ya bayyana cewa, zaben Abdullahi Mohamed Farmajo a matsayin sabon shugaban kasar Somaliya, wata kyakkyawar dama ce ta bude sabon babin tabbatar da zaman lafiya da ci gaban kasar.

Madeira ya bayyana hakan ne cikin sharhin da jaridar Daily Nation ta kasar Kenya ta wallafa, yana mai cewa, zaben shugaba Farmajo zai taimakawa kasar Somaliya ta mance da abubuwan tashin hankalin da suka faru a baya a cikin kasar.

Kasar Somaliya ta shafe shekaru da dama tana fuskantar rashin kwanciyar hankali, da matsalar fari da tashin hankali mai nasaba da tsattsauran ra'ayi, matsalolin da jami'in na AU ya ce za su kasance tarihi biyo bayan zaben shugaban kasar da ya gudana cikin nasara.

Abdullahi Farmajo dai ya kayar da shugaban kasar mai ci Hassan Sheikh Mohamud a zaben shugabancin kasar da aka gudanar.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China