in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masanin tattalina arziki a kasar Ghana ya bukaci Sin ta zuba jari a fannin noma da masana'antu
2017-02-15 09:31:49 cri
Farfesa Ernest Aryeetey, wani masanin tattalin arzikine a kasar Ghana, ya bukaci gwanmatin kasar data gayyato masu zuba jari a fannin aikin gona da masana'antu daga kasar Sin domin habaka tattalin arzikin kasar da kuma samar da ayyukan yi.

Masanin tattalin arzikin wanda tsohon mataimakin shugaban jami'ar Ghana dake Legon ne, ya bayyana aikin gona a matsayin wani muhimmin fannin wanda za'a iya bunkasa shi cikin karami da matsakaicin zango, kana ya jaddada muhimmancin bunkasa fannin masana'antu wanda galibi yake daukar dogon lokaci.

Ernest ya bayyana a lokacin wani taro da masu ruwa da tsaki a harkokin kasuwanci a birnin Accra cewa, inganta fannin masana'atun yana da matukar alfanu, bama wajen sarrafa kayan amfanin gona kadai ba, har ma da sauran kayayyakin da ake sayo su daga kasashen ketare a halin yanzu.

Aryeetey yace, game da batun manyan fasahohin da ake bukatar amfani dasu a masana'antun kasar, a cewarsa gwamnatin Ghana zata hada kai da kamfanonin kasashen Sin da Indiya wadanda a shirye suke a koda yaushe su zuba jari a masana'antun kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China