in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An tsinci gawarwaki sama da 70 a Sirte, inji kungiyar bada agaji ta Libyan Red Crescent
2017-02-13 09:28:31 cri
Jami'an kungiyar bada agaji ta Red Crescent ta Libya ta ce an gano gawarwakin mutane sama da 70 a yankin Sirte cikin kwanaki 10 da suka gabata.

Saleh Bozreba, jagoran kungiyar ta Red Crescent mai yunkurin wanzar da zaman lafiya a Misrata, yace, gawarwaki 65 daga cikin adadin da aka gano, mayakan kungiyar IS ne, wadan da aka kashe a sanadiyyar hare hare ta sama da jiragen yakin Amurka suka kaddamar a ranar 19 ga watan Janairu a kudancin Sirte.

Bozreba yace har yanzu jami'an sa kai na kungiyar Red Crescent suna cigaba da aikin gano ragowar gawarwakin a Sirte, sai dai ya bukaci kungiyoyin kasar Libya da na kasa da kasa da su agazawa tawagar.

Sirte, nada tazarar kilomita 450 dake gabashin Tripoli babban birnin kasar, kuma ya kasance a hannun mayakan IS sama da shekara guda kafin daga bisani dakarun dake biyayya ga gwamnatin Libya mai samun goyon bayan MDD su kwace ikon birnin bayan shafe watanni 7 suna gwabza yaki.

Rikicin ya haddasa mutuwar da kuma raunatar daruruwan jami'an gwamnati.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China