in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Ghana ya rantsar da sabbin ministocinsa
2017-02-08 19:23:28 cri
Shugaba Nana Akufo-Addo na kasar Ghana ya bukaci sabbin ministocinsa da su yi aiki tukuru don ganin an samar da ci gaba da kuma makoma mai haske a kasar.

Shugaba Addo ya yi wannan kiran jiya da dare lokacin da ya ke rantsar da ministoci 12 da majalisar dokokin kasar ta tantace don nada su mukaman ministoci.

Ya kuma shaidawa ministocin cewa, al'ummar Ghana sun dora fatansu a kan jam'iyyar NPP wajen farfado da yanayin jin dadin jama'a da tattalin arzikin kasar, wadanda za su kai ga ci gaban kasar ta Ghana.

Bikin rantsar da sabbin ministocin na zuwa kwanaki 11 bayan da aka rantsar da rukuni na 1 mai kunshe da minsitoci 13 a watan da ya gabata. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China