Da yake jawabi ga sabbin ministocin a daren Juma'ar da ta gabata, Akufo-Addo ya ce rantsar da ministocin babban nauyi ne musamman bisa la'akari da irin amincewar da alummar Ghana suka nuna na neman sauyin gwamnati da salon yadda ake tafiyar da harkokin tattalin arzikin kasar.
Shugaban na Ghana ya bukaci sabbin ministocin da su kare manufofin gwamnati kana su yi taka tsantsan wajen tafiyar da dukiyar kasa. (Ahmad)