in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ronaldinho ya ki zuwa Coritiba
2017-02-08 17:02:17 cri
Shahararren dan wasan kwallon kafa wanda ya taba lashe kofin duniya tare da kasar Brazil wato Ronaldinho, ya ki yarda da gayyatar da kulob din Coritiba ya yi masa, lamarin da ya sa ake hasashen cewa, watakila dan wasan zai yi ritaya daga buga gasannin wasan kwallon kafa baki daya.

Kulob din Coritiba karkashin tsarin Serie A na kasar Brazil, ya sanar da cewa, ba zai ci gaba da neman Ronaldinho ba, bisa la'akari da yadda dan wasan ya karbi matsayin da kulob din Barcelona ya ba shi, na kasancewa jakadan kulob din. Ya ce irin alakar dake tsakanin Ronaldinho da kulob din Barcelona zai yi tasiri matuka kan ajandar dan wasan a nan gaba.

Dan wasan mai shekaru 36 a duniya ya dade ba ya takawa wani kulob wasa, tun bayan da ya bar kulob din Fluminense dake birnin Rio de Janeiro a watan Satumban shekarar 2015.

Bisa sabon matsayinsa na jakadan Barcelona, ana saran ganin dan wasan, wanda ya taba zama dan wasa mafi kwarewa a duniya har karo 2, yana zagaya sassan duniya, domin halartar bukukuwa daban daban, a wani mataki na bullo da hanyoyin kara daukaka matsayin FC Barcelona a idanun al'ummun duniya. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China