in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar Burkina Faso ta zama ta uku a gasar cin kofin nahiyar Afirka
2017-02-05 13:18:41 cri
A Jiya Asabar aka gudanar da wasan neman matsayi na 3 tsakanin kungiyoyin Burkina Faso da Ghana a gasar cin kofin nahiyar Afirka ta wasan kwallon kafa ta shekarar 2017, wadda ke gudana a kasar Gabon. A wajen wasan, Alain Traore ya buga kwallon cikin raga, ta yadda ya taimakawa kungiyarsa ta Burkina Faso ta doke kungiyar wasan Ghana da ci 1 da nema. Hakan yasa Burkina Faso ta samu matsayi na 3 a gasar cin kofin nahiyar Afirka a wannan karo.

Kungiyar ta Burkina Faso ta taka rawar a-zo-a-gani a gasar ta bana, inda ta lashe dukkan wasannin da aka buga a zagayen rukunin wasan, ta zarce zuwa zagaye na gaba bisa matsayi na farko data samu a rukuninta. Daga baya kuma, a wasan kusa da na karshe, Burkina Faso ta yi kunnen doki da Masar da ci 1 da 1 cikin wa'adin wasan na mintuna 90, sai dai a karshe Masar ta zara tata kwallon a bugun daga kai sai mai tsaron gida.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China