in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ronaldinho na shirin komawa tamaula
2017-01-18 15:52:03 cri
Dan wasan da hukumar FIFA ta baiwa lambar yabo ta kasancewa dan wasa mafi hazaka har karo biyu, kuma dan asalin kasar Brazil Ronaldinho, na fatan komawa taka leda a bana, bayan da ya shafe shekara guda ba tare da ya bugawa wata kungiyar waje wasa ba, kamar dai yadda dan uwansa kuma manajan sa Roberto Assis ya bayyana.

Assis ya bayyana cewa, Ronaldinho mai shekaru 36 da haihuwa, na fatan bugawa daya daga kulaflikan da ke buga gasar Copa Libertadores kwallo ne. Cikin su kuwa akwai Chapecoense ko Coritiba na Brazil, ko kuma kungiyar Nacional ta Uruguay.

A wata zantawa da ya yi da jaridar kasar Uruguay mai suna El Pais, Assis ya ce "burin mu shi ne ya buga wasa a wannan shekara ta 2017. Bayan hutu na shekara guda, wanda ya ba mu damar kewaya duniya muka kuma kara fahimtar kasashe da a baya bamu taba sani ba".

Game da yiwuwar bugawa kungiyar Nacional wasa, Assis ya ce a madadin Ronaldinho, sun zanta da wakilan kungiyar, ko da yake ba a kai ga daddale wani kuduri ba tukuna.

Ronaldinho dai ya sha hutu tun bayan da ya rabu da kungiyar Fluminense ta Brazil a watan Satumbar bara. Sai dai a lokacin da yake hutun, ya taba halartar wasu bukukuwa a Peru, da Ecuador, da Guatemala, da Amurka da kuma Sin. Ya kuma halarci gasar futsal da aka buga a kasar India.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China