in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwmaitin sulhu na MDD ya tsawaita wa'adin sanya takunkumi ga wadanda suka lalata kwanciyar hankalin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya
2017-01-28 13:28:47 cri
Jiya Jumma'a ne, kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya zartas da wani kuduri, inda ya tsawaita wa'adin takunkumi ga duk mutanen da suka lahanta kwanciyar hankali a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, da shekara guda, wato zuwa ranar 31 ga watan Janairun badi.

Kudurin ya bukaci kasashe daban-daban da su dauki duk wani matakin da ya wajaba, na kakabawa duk wadanda suka kawo illa ga zaman lafiya da kwanciyar hankali da tsaro a kasar Afirka ta Tsakiya takunkumin haramta sayar musu makamai da yin tafiye-tafiye, da kuma sanya musu haramcin yi amfani da kudadensu a banki.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China