in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin saman Nijeriya, ta fara bincike kan harin da aka kai sansanin 'yan gudun hijira bisa kuskure
2017-01-20 10:46:27 cri
A jiya Alhamis ne, rundunar sojin saman Nijeriya, ta ce ta fara bincike kan harin da jirgin yakinta ya kai kan sansanin 'yan gudun hijira bisa kuskure a farkon wannan makon, al'amarin da ya yi sanadin mutuwar fararen hula da dama a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar.

Kakakin rundunar, Ayodele Famuyiwa, ya ce za a gudanar da binciken ne domin kare sake aukuwar lamarin, tare da sanin dalilai da kuma abubuwan da suka janyo kai harin.

Mutane akalla hamsin da biyu ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu dari da ashirin suka jikkata, a harin da tuni rundunar sojin ta ayyana a matsayin kuskuren aiki.

Rundunar sojin Nijeriya ta ce al'amarin ya auku ne, bayan ta samu wani rahoton sirri dake cewa, 'yan kungiyar Boko Haram na sake hade kansu a garin da sansanin yake.

Har ila yau, Ayodele Famuyiwa, ya ce rundunar sojin saman ta kafa wani kwamiti mai kunshe da manyan hafsoshi, domin gudanar da bincike kan harin, baya ga shaidun gani da ido ashirin da ake da su.

Sannan, an ba ayarin masu binciken damar gayyatar duk wanda ke da shaida kan al'amarin, inda ya ce, kwamitin zai mika rahotonsa ranar ko kafin 2 ga watan Fabreru mai zuwa.(Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China