Musulmin kasar Burundi sun janye jiki a ranar Laraba tare da 'yan uwansu musulmai dake zuwa sansanonin horo domin kungiyar IS. Mun sami labari nan da kuma can cewa 'yan kasar Burundi musulmi na zuwa sansanonin bada horo domin shiga kungiyar IS, in ji shugaban kungiyar addinin musulunci ta kasar Burundi (COMIBU), Cheik Sadiki Kajandi, a yayin wani zaman taro a birnin Bujumbura da ya hada dukkan limamai da malaman wa'azi domin karfafa zaman lafiya. (Maman Ada)