in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta kudu ta musanta ikirarin da dakarun 'yan tawaye suka yi na kame garuruwa 3
2016-11-18 11:13:03 cri
Sojojin gwamnatin Sudan ta kudu sun karyata ikirarin da mayakan 'yan tawayen kasar dake goyon bayan hambararren mataimakin shugaban kasar Riek Machar suka yi, na karbe ikon wasu garuruwa 3 a kudu maso yammaci da arewacin kasar.

Mai magana da yawun sojin Sudan ta kudun Santo Dominic Chol, ya tabbatarwa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewar, ana fama da rikice rikice a sassa daban daban na kasar, amma ya musanta ikirarin da dakarun dake biyayya ga Machar suka yi na kwace ikon wasu garuruwa a kasar.

Ya ce a cikin yan makonnin nan, mayakan na SPLM-IO suna cigaba da zafafa hare hare kan yankunan dake karkashin ikon gwamnatin kasar.

A ranar Larabar da ta gabata ne, mai magana da yawun SPLM-IO Dickson Gatluak, ya yi ikirarin cewa dakarunsu sun kwace iko a Bazi, yankin dake kan iyakar Sudan ta kudu da jamhuriyar dimokaradiyyar Congo, da Morobo a tsakiyar jahar Equatoria, sai kuma Kaljak a jahar hadin kai.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China