in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta koka game da tabarbarewar al'amurra wanda ya hana kai agaji a Sudan ta kudu
2016-12-09 13:15:25 cri
Hukumar kula da 'harkokin jin kai ta MDD ta nuna damuwa game da tabarwabarewar al'amurra da ke haddasa tafiyar hawainiya game da kai kayan agaji ga mabuka a Sudan ta kudu, hukumar tana mai cewa, akwai matsaoli sama da guda 100 da aka samu a cikin watan Nuwamba kadai, kuma shi ne adadin mafi yawa da aka taba samu cikin wata guda kacal tun a watan Yunin shekarar 2015.

A cewar ofishin bada agaji na MDD OCHA, daga cikin matsalolin aikin kai agajin 100 da aka samu a watan Nuwamba, kashi 66 cikin 100 ya shafi cin zarafin jami'an aikin bada agaji ne ko kuma kayayyakin agajin, yayin da kashi 26 cikin 100 ya shafi matsaloli ne game da tsare tsaren kai agajin, biyar daga ciki ya shafi batun yin katsalandan ne game da yadda ma'aikatan ke tafiyar da ayyukansu, bakwai kuma ya shafi yadda ake aza haraji ba bisa ka'ida ba, sannan biyu daga ciki ya shafi yadda ake kwace aikin rabon agajin daga hannun jami'an da abin ya shafa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China