in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan sandan Turkiyya sun kama mutane 8 da ake zarginsu da kai hari kasar
2017-01-03 09:55:46 cri
Rahoto daga kafofin watsa labaran kasar Turkiyya ya ce, jiya Litinin, 'yan sandan kasar sun kame mutum 8 da ake zargi da kai harin ta'addanci wani gidan rawa da sanyin safiyar Lahadi, 1 ga wata a birnin Istambul.

Sai dai 'yan sandan ba su bayyana ainihin su wanene ba.

A wani labarin kuma, Jaridar Hürriyet ta Turkiyya ta ruwaito cewa, kungiyar IS ta sanar da daukar alhakin kai harin a jiya Litinin.

Da sanyin safiyar ranar 1 ga wata ne, wani dan bingida ya kutsa kai cikin wani gidan rawa mai suna Reina, dake cibiyar birnin Istambul, inda ya yi harbin kan mai uwa da wabi, kan wadanda ke bikin sabuwar shekara.

Daga bisani dai dan bindigar ya tsere, amma a halin yanzu 'yan sanda sun dukufa domin farautarsa.

A wata sabuwa kuma, ma'aikatar harkokin cikin gidan Turkiyya ta sanar da cewa, a cikin makon daya da ya shude, 'yan sandan kasar sun tasa keyar mutane 47 da ake zargin suna da alaka da kungiyar IS, ciki har da wasu 25 wadanda aka riga aka cafke su.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China