in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yunkurin juyin mulki a Turkiyya ya haddasa mutuwar mutane 194, tare cafke sojoji 1563
2016-07-16 17:32:55 cri
A daren Jumma'a 15 ga wata, wasu sojojin kasar Turkiyya sun yi yunkurin kifar da gwamnati. Umit Dundar, mukadashin babban hafsan hafsoshin rundunar sojin kasar Turkiyya ya sanar da cewa, ya zuwa ranar Asabar 16 ga wata, mutane 194 sun rasa rayukansu, ciki har da 'yan sadan 41, fararen hula 49 da 'yan tawaye 104. Haka kuma, gwamnatin Turkiyya ta riga ta cafke sojoji 1563 wadanda suke da hannu kan yunkurin juyin mulki. Ko da yake gwamnatin kasar ta sanar da cewa, ta ciwo kan halin da ake ciki yanzu, amma har yanzu ana jin karar bindigogi. A sanyin safiyar Asabar, shugaba Recep Tayyip Erdogan na kasar ya bayyana a birnin Istanbul, cewar zai kawar da dukkan wadanda suka yi yunkurin juyin mulkin daga cikin rundunar soja.

Bayan wasu 'yan sa'o'in da wasu sojoji suka nemi kifar da gwamnatinsa, shugaba Erdogan wanda yake hutu a garin Marmaris dake bakin teku a kudu maso yammacin kasar ya dawo birnin Istanbul, tare da samun kyaukyan tarbo a filin jiragen sama.

A yayin wani taron manema labaru da aka shirya jim kadan, Mr. Erdogan ya zargi lamarin yunkurin juyin mulki cewa, "lamari ne na namen ta da zaune tsaye" da "cin amana". Ya ce, zai kawar da dukkan wadanda suka yi wannan yunkurin juyin mulki daga rundunar sojan kasar gaba daya. Sannan, shugaba Erdogan ya zargi Fetura Gulen, wani dan Turkiyya wanda ke gudun hijira a kasar Amurka da jagoranta wannan makarkashiya, kuma shugaba Erdogan ya kira ga jama'ar kasar da su fito kan tituna su yi zanga-zanga domin nuna goyon bayan gwamnati mai ci. Bugu da kari, ya nemi sojoji kada su bude wuta kan 'yan uwansu da kasarsu ta asili.

Bisa labari daban da aka bayar, an ce, firayin ministan kasar Turkiyya Bina Le Yıldırım ya nemi 'yan majalisar dokokin kasar da su shirya wani taron gaggawa domin tinkarar hargitsin da ake fama da shi a kasar.

Game da halin ta da zaune tsaye da ake ciki a kasar Turkiyya, Mr. Lu Kang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana cewa, kasar Sin na mai da hankalinta sosai kan halin da ake ciki a kasar Turkiyya, tana fatan za a iya maido da oda da kwanciyar hankali a kasar Turkiyya cikin sauri. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China