in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Keqiang ya aikawa shugabar gwamnatin kasar Jamus Merkel sakon ta'aziyya
2016-12-22 10:12:28 cri
A jiya Laraba ne, firaministan kasar Sin Li Keqiang ya aikawa shugabar gwamnatin kasar Jamus Angela Merkel sakon ta'aziyya game da harin ta'addanci da aka kai wata kasuwa dake birnin Berlin na kasar Jamus.

A cikin sakon, Li Keqiang ya kadu a samu labarin harin ta'addanci da aka kai birnin Berlin a daren ranar 19 ga wata, harin da ya haddasa mutuwa tare da raunata mutane da dama. A madadin gwamnatin kasar Sin, Li Keqiang ya mika ta'aziyya ga iyalan mutanen da suka mutu a sakamakon harin, sannan ya jajantawa iyalan wadanda suka jikkata, tare da fatan samun sauki ga mutanen da suka ji rauni. Sin tana goyon bayan kasar Jamus a kokarin da take yi na yaki da ta'addanci da tabbatar da tsaron kasa, kana yana son kara yin hadin gwiwa tare da kasar Jamus da sauran kasashen duniya a kokarin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya baki daya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China