in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya yana da kyakkyawan fata na magance matsin tattalin arzikin kasar a 2017
2016-12-20 09:37:15 cri

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana a jiya Litinin cewa, yana da kyakkyawan fata cewa, halin matsin tattalin arziki da kasar ta shiga zai zo karshe a shekarar 2017 mai kamawa.

Shugaban ya bayyana hakan ne a Abuja, fadar mulkin kasar, a lokacin da ya jagoranci bude taron bita wanda ma'aikatar harkokin wajen kasar ta shiryawa jami'an ofisoshin jakadancin kasar.

Shugaba Buhari ya bayyana kwarin gwiwa cewa, dalilan da suka haddasa matsin tattalin arzikin kasar, za'a dakile su a shekarar mai kamawa.

A cewarsa, halin komadar tattalin arzikin da kasar ke fama da shi ya sanya kasar yin wasu sauye sauye game da manufofinta na hulda da kasashen ketare.

Ya bukaci jakadun Najeriyar a kasashen waje, da su aiwatar da kyawawan manufofi wadanda za su daga kimar kasar a kasashen waje, kana su ba da gudunmowarsu wajen ci gaban Najeriya a yayin mu'amala da kasashen duniya.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China