in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban majalisar dokokin jama'ar Togo ya gana da mataimakiyar direktan hukumar kula da harkokin cudanya da jam'iyyun siyasa na waje na kwamitin tsakiyar JKS na Sin
2016-12-20 09:28:03 cri
Jiya Litinin, shugaban majalisar dokokin jama'ar kasar Togo Dama Dramani ya gana da tawagar sada zumunta ta jam'iyyar kwaminis ta Sin da mataimakiyar direktan hukumar kula da harkokin cudanya da jam'iyyun siyasa na kasashen waje na kwamitin tsakiyar JKS na Sin wadda Xu Lvping ke jagoranta a birnin Lome, fadar mullkin kasar Togo.

Dramani ya bayyana cewa, Togo da Sin suna da dadadden tarihi na sada zumunta, Togo ta dora muhimmanci sosai kan dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin, kana tana fatan hada kai tare da kasar Sin, ta yadda za a samun sabon sakamako a hadin gwiwar da ke tsakaninsu a fannoni daban daban.

A nata bangare, Xu Lvping ta bayyana cewa, jam'iyyar kwaminis ta Sin tana son hada kai tare da jam'iyyar Rally for the Republic, ta yadda za a aiwatar da ayyukan da shugabannin kasashen biyu suka cimma daidaito, da sa kaimi ga bunkasa hadin gwiwarsu.

A yayin ziyararta, Xu Lvping ta yi shawarwari tare da shugabannin jam'iyyar Rally for the Republic dake kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China