in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Halartar Afrika ga musanyar kayayyakin da ake kerawa a duniya na wakiltar kawai kashi 1.9 cikin 100 a duniya
2016-11-24 10:49:38 cri
Ministar kasuwanci, masana'antu da bunkasa bangaren masu zaman kansu da yawon bude ta kasar Togo, Bernadette Legzim-Balouki, ta bayyana rashin jin dadinta a ranar Laraba kan abin mamakin da ke cigaba da faruwa a dukkan Afrika, na cewa nahiyar da kunshe da dimbin albarkatun ma'adinai da na noma, amma abin bakin ciki shi ne harlatar Afrika ga musanyar kayayyakin da ake kerawa na wakiltar kawai kashi 1.9 cikin 100 a duniya.

Madam Legzim-Balouki ta yi furucin a yayin bikin ranar masana'antu ta Afrika da aka gudanar a ranar 20 ga watan Nuwamba bisa taken wannan shekara "zuba jari na shekaru goma na uku na cigaban masanasa'antu domin Afrika: Kalubaloli da dabarun samun moriya". Ministar ta tunatar cewa dandalin masana'antu na kungiyar ECOWAS, da aka gudanar a birnin Accra na kasar Ghana a ranar 21 ga watan Yuli ya bukaci kasashe mambobi na gamayyar dasu karfafa asusun musammun na ajiya domin kara halartar shiyyar ga musanyar kayayyakin da ake kerawa a duniya.

Game da wannan, ta nuna yabo ga shugaban kasar Togo, Faure Gnassingbe, wanda bai jira ba domin yin kira da a kafa wata cibiyar kasa ta bunkasa da tabbatar da ajiyar zuba jari domin musammun ma bunkasa kananan masana'antu da matsakaita (PME/PMI) domin matasa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China