in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe da dama sun sake jaddada bin manufar "kasar Sin daya tak a duniya"
2016-12-15 19:27:46 cri
Jiya Laraba, ministan harkokin wajen kasar Faransa Jean-Marc Ayrault ya sake jaddada manufar "kasar Sin daya tak a duniya" yayin da yake tsokaci kan kalaman da shugaban kasar Amurka mai jiran gado Donald Trump ya yi kan batun yankin Taiwan na kasar Sin.

A yau kuma, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya yaba wa Mr. Ayrault dangane da goyon bayan manufar "kasar Sin daya tak a duniya".

Ban da wannan kuma, manyan jami'an kasashen Jamus da Australia da dai sauransu sun bayyana aniyarsu ta kare manufar "kasar Sin daya tak a duniya". Dangane da wannan lamari, Geng Shuang ya bayyana cewa, tabbatar da manufar "kasar Sin daya tak a duniya" shi ne muhimmin tushen raya dangantarkar abokantaka a tsakanin kasar Sin da sauran kasashen duniya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China