A yau ne mahukuntan kasar Sin suka bukaci kasar Singapore da ta martaba manufar kasar Sin daya tak a duniya. Wannan kira na zuwa bayan da ma'aikatan kwastan a yankin Hong Kong na kasar Sin suka damke wasu motocin kasar Singapore masu sulke guda 9 da aka ba da rahoton cewa, an yi amfani da su wajen rawar daji a yankin Taiwan a makon da ya gabata.
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya shaidawa manema labarai cewa, kasar Sin ba ta goyon bayan duk wata hulda a hukumance tsakanin yankin Taiwan da duk wata kasa da ta kulla huldar diflomasiya da kasar Sin, ciki har da musaya da hadin gwiwar sojoji.(Ibrahim)