in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin waje na kasar Sin ya yi sharhi a kan tattaunawar da Donald Trump ya yi tare da jagorar yankin Taiwan
2016-12-04 13:35:16 cri
A game da labarin tattaunawa ta wayar tarho da zababben shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi tare da shugabar yankin Taiwan Tsai Ing-wen, ministan harkokin waje na kasar Sin Wang Yi a jiya Asabar ya bayyana cewa, wannan wani makirci ne na bangaren Taiwan, wanda ko kadan ba zai iya canza yanayin da ake ciki a duniya na kasancewar Sin, kasa daya tak a duniya.

Ministan ya kara da cewa, "A ganina, wannan ma ba zai iya canza manufar da gwamnatin kasar Amurka ta dade take dauka kan kasancewar kasar Sin daya tak a duniya, manufar da ta zama tushe na bunkasa huldar da ke tsakanin kasashen biyu, kuma ba ma so a lalata wannan tushe na siyasa."

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China