Zhang Dejiang ya bayyana cewa, majalisar wakilan jama'ar kasar Sin tana son kara yin hadin gwiwa tare da majalisar wakilai da ta dattijai ta kasar Gabon ta yadda za a bunkasa dangantakar dake tsakanin Sin da Gabon a dukkan fannoni.
A nasa bangare, shugaba Bongo ya yabawa kasar Sin bisa ga goyon bayan da ta ke nunawa ga batun raya Afirka, yana fatan ta wannan ziyara, kasashen biyu za su kara inganta hadin gwiwar dake tsakaninsu a fannonin tattalin arziki da cinikayya da hadin gwiwa. (Zainab)