Bayan nasasar Ali Bongo da ta janyo cece kuce da ma'aikatar cikin gida ta sanar a cibiyar hukumar zabe mai zaman kanta ta CENAP a ranar 31 ga watan Augusta, babban dan adawar nan Jean Ping ya gabatar da kara inda ya nemi da a sake kidayar kuri'un zabe na kowace rumfar zabe, musammun ma a yankin Haut-Ogooue, inda Ali Bongo ya samu kashi fiye da 95 cikin 100 na kuri'un da aka jefa, tare da kashi fiye da 99 cikin 100 na halartar zaben. (Maman Ada)