in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Togo da Zambiya na tattauna goyon bayan junansu domin muhimman kujeru 2 a zaben AU
2016-12-06 10:42:56 cri

Shugaban kasar Togo Faure Gnassingbe ya tattauna a ranar Litinin a birnin Lome tare da Dora Siliya, ministar noman kasar Zambiya, kan matakan da za su dauka domin ganin cewa, takarar Togo kan kujerar komishinan harkokin tattalin arziki na kwamitin tarayyar Afrika (AU), da kuma takarar Zambiya kan kujerar kwamishinan kasuwanci, masana'antu da noma, sun sami nasara a yayin zabukan watan Janairu mai zuwa.

A cikin watan Janairun shekarar 2017, kungiyar AU za ta zabi wani sabon shugaban kwamitin domin maye gurbin 'yar kasar Afrika ta Kudu, madam Nkosazana Dlamini Zuma. Sabon mutumin da zai tafiyar da aikinsa tare da taimakon wani mataimakin shugaba, da kuma wasu kwamishinoni guda takwas. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China