in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya tana binciken mutuwar mutumin da ya yi satar shiga jirgin Arik
2016-12-02 10:31:49 cri
Gwamnatin kasar Najeriya a jiya Alhamis ta sanar da cewa, an riga an fara bincike kan lamarin mutuwar mutumin da ya yi satar shiga jirgin saman Arik Air, wanda aka gano gawarsa a filin saukar jiragen sama na Afirka ta Kudu.

Ana gudanar da binciken ne bisa hadin gwiwa da kamfanin Arik Air, da hukumomin kasar Afirka ta Kudu, in ji Sam Adurogboye, kakakin hukumar zirga-zirgar jiragen sama ta NCAA, wanda ya fadi haka a birnin Ikko. Ya kuma kara da cewa, bayan da aka kammla binciken, gwamnatin kasar za ta dauki matakin da ya wajaba, sai dai har yanzu ba a san wane ne wannan mutum da ya rasa ransa.

A nasa bangaren, kamfanin Arik Air shi ma ya ce, ba shi da wani bayani dangane da batun, sai bayan da aka kammala binciken lamarin.

An gano gawar mutumin ne a ranar Laraba, a cikin rijiyar wili na wani jirgin saman kamfanin Arik mai samfurin A330-200, bayan da jirgin ya sauka a filin saukar jiragen sama na Oliver Tambo da ke birnin Johannesburg na kasar Afrika ta Kudu.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China