in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojan kasar Iran ta ce ba ta da shirin tura sojojinta zuwa wajen yakin 'yantar da birnin Mosul
2016-11-25 20:30:23 cri
A jiya Alhamis ne, babban kwamandan rundunar sojan 'yantar da jumhuriyar musulunci ta Iran janar Mohammad Ali Jafari ya musunta labarin da wasu kafofin yada labaru suka bayar, cewa kasar Iran ta tura sojojinta zuwa yakin 'yantar da birnin Mosul na kasar Iraki. Janar Jafari ya bayyana cewa, kasar Iran ba ta tura sojojinta domin taimakawa kasar Iraki a fafatawar da ake yi na 'yantar da birnin Mosul daga hannun kungiyar IS ba.

A watan Oktoban da ya gabata ne, jaridar "The Huffington" ta kasar Amurka ta wallafa wani labarin da ke cewa, kasar Iran za ta tura sojojinta zuwa kasar Iraki domin 'yantar da birnin Mosul. Game da labarin, Mr. Ali Akbar Velayati, mai ba da shawara ga shugaban koli na Iran, kana tsohon ministan harkokin wajen kasar Iran ya taba bayyana a ran 19 ga watan Oktoba, cewar kasar Iran ba za ta tura sojojinta zuwa kasar Iraki domin 'yantar da birnin Mosul da ke hannun IS, amma ta ba da wasu shawarwarin soja kawai kamar yadda gwamnatin kasar Iraki ta bukata. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China